Kamfanin dillancin labaran iqna, ya bayar da rahoton cewa, a lokacin da yake amsa tambayoyin manema labarai a jiya birnin Doha fadar mulkin kasar Qatar, ministan harkokin wajen kasar Qatar Muhammad Bin Abdulrahman Al Thani ya bayyana cewa, takunkuman da Amurka ta kakaba wa Iran suna da mummunan tasiri ga kasashe masu danyen man fetur.
Ya ce matakin da Amurka ta dauka bai dace ba, domin kuwa ko shakka babu wannan takunkumi ba kasar Iran kawai zai cutar ba kamar yadda Amurka take tsammani, hakan zai cutar da dukaknin kasashen masu sayen danyen mai daga Iran, da kuma masu sayen mai a kasuwanninsa na duniya.
Ministan na Qatar ya ce kasarsa ba za ta yi aiki da takunkumin na kasar Amurka a kan kasar Iran ba.