IQNA

Albashir ya Sake Gurfana A Gaban Kuliya A Karo Na Biyu

23:03 - August 24, 2019
Lambar Labari: 3483983
Bangaren kasa da kasa, hambararren shugaban kasar Sudan Umar Hassan Albashir ya sake gurfana agaban kuliya domin fuskantar shari'a.

Kamfanin dillancin labaran iqna, An kammala sauraron shir’ar da akewa tsohon shugaban kasar Sudan Umar Hassan Al-Bashir a karo na biyu a yau Asabar a wata kotu a birnin Khartun babban birnin kasar, sannan an sanya ranar 31 ga watan da muke ciki a matsayin ranar da za’a saurari shari’ar a karo na ukku

Tsohon shugaban na Sudan ya sami halartar zaman shari’ar a karo na biyu a yau Asabar da kansa, sannan shugaban tawagar lauyoyi 130 masu kare shi mai suna Ahmad Ibrahim Tahir ya bayyana cewa sun gabatarwa kotun bukatar a bada belin tsohon shugaban kasar a zamanta na yau.

A ranar litinin da ta gabata ce aka gurfanar da tsohon shugaban kasar a gaban kotu a karon farko, kuma tawagar masu gabatar da kara wacce ta kunshi lauyayoyin gwamnati 7 ne suka karantawa tsohon shugaban kasar tuhume-tuhumen da ake masa, wadanda suka hada da kashe masu zanga-zanga da kuma ajiye kudade kasashen waje a gidansa.

Sai kuma a zaman sauraron shari’ar a yau Asabar lauyoyi masu gabatar da kara sun gabatar da shaidu guds 3 wadanda suka binciki gidan tsohon shugaban kasan bayan an yi masa juyin mulki, akwai sauran masu bada shaida wadanda za’a gabatar a zaman sauraro shari’ar nan gaba.

Har’ila yau wasu daga cikin dangin tsohon shugaban kasar sun sami halartar zaman shari’arsa ta yau Asabar, sannan wasu mago bayansa kuma sun yi gangami a gaban kotun inda suke yin allawadai da shari’ar da ake masa.

3837083

 

captcha