Bayanin ya ci gaba da cewa bisa ga al'ada wannan taro nana gudanar da shi a kowace shekara, domin yin juyayi da alhini kan wafatin manzon rahma tsira da amincin Allah su tabbata gare shi da iyalan gidansa tsarkaka.
Baya ga dora tuta kan tulluwar hubbaren mai tsarki, ana gabatar da jawabai da suka shafi rayuwar ma'aiki da kuma kissoshi da suka shafi wafatinsa da wasicinsa.
Bisa ga ruwayoyi ad suka inganta daga ahlul bait (AS) manzon Allah (SAW) ya rasu ne a ranar 28 ga watan safar shekara ta 11 bayan hijira, kuma dan uwansa Imam Ali (AS) ne ya jagoranci janazarsa.