Kamfanin dillancin labaran iqna, Shugaban kasar Iran, Dakta Hassan Rohani, ya kudiri anniyar gabatar da wani shiri kan tsaro a yankin Golf da zai shafi, mashigar ruwa ta Hormoz da kuma tekun Oman a gaban babban zauren taron MDD da za’a faraway a makon gobe.
Dakta Rohani, na bayyana hakan ne, a cikin jawabin da ya gabatar yau, yayin da yake halartar bikin faretin sojojin kasar na zagayowar cika shekaru 39 na makon tsaron kasa.
A cikin jawabin da ya gabatar tun daga hubaren mirigayi Imam Khomaini, wanda ya asasa jamhuriya musulinci ta Iran, shugaba Rohanin, ya yi alkawarin cewa a cikin kwanaki masu zuwa gaban taron koli na MDD, zai gabatar da wani shiri na karfafa tsaro a yankin, golf da mashigar Hormuz da kuma tekun Oman, wanda a cewarsa kasancewar dakarun ketare a yankin zai iya kasancewa barazana ga tsaron harkokin mai da na makamashi a duniya da kuma jiragen ruwa na dakon main a kasa da kasa.
Shugaba Ruhani ya kara da cewa, duk inda Amurka ta sanya kafa, to tana haifar da matsalar tsaro ne, a daidai lokacin da dakarun Iran din a cewarsa suke kokarin tabbatar da tsaro.
A daya bangare kuma shugaba Rohani, ya ce a shirye su ke a koda yaushe domin kulla zaman lafiya da kasashe makobtan Iran a daidai wannan lokaci mai cike da zaman tankiya, kuma zamu ma iya yi wa makiyanmu a yankin yafiya, a daidai lokacin da Amurka da yahudawan sahayoniya ke neman cin moriyar halin da ake ciki na rarabuwar kai.