Kamfanin dillancin labaran iqna, jaridar ta Guardian ce ta bayyana haka a jiya Litinin, inda ta nakalto Boris Jonson yana fadar cewa addinin musulunci, addinin koma baya ne ga ga al-ummar duniya.
Amma kamfanin Tell MAMA wanda yake aikin lissafa mizanin kiyayyar da musulmim suke fuskanta a kasar Britania, ya bayyana cewa maganganun na Boris Jonson sun nuna cewa ya jahilci addinin musulunci.
Banda haka wasu rahotannin sun bayyana cewa kashi 52% na yan majalisar dokokin kasar Britania sun jahilcin matsayin da addinin musulunci ya ke da shi a tarihin bil’adama.
Kafin furucinsa na bayan bayan nan dai, Boris Jonson ya taba sifanta mata musulmi masu sanya hajibi a matsayin barayin banki.
Masana suna ganin da alamun idan Jonson ya haye kan kujerar Firai ministan kasar Biritania, yana iya kara takurawa musulman kasar.