Bayanin kungiyar ya ce rashin sakin malamin wata manuniya ce a kan yadda doka bata aiki a Najeriya, kuma alamu ne da ke nuni da cewa an kama hanyar kama karya Kenan maimakon mulkin dimokradiya wanda al'umma suka zabi gwamnati dominsa.
Bayanin ya ce duk da cewa gwamnatin Kaduna da kanta ta tabbatar da kasha daruruwan magoya bayan malamin da sojoji suka yi a gidan malamin a lokacin da suka kame shi, amma har yanzu ba hukunta koda wani jami'in soji guda kan hakan ba.
Ita ma a nata bangaren kungiyar Amnesty International ta jadda kiranta ga mahukuntan Najeriya da su saki malamin, kuma a hkunta duk wanda yake da hannu a kisan gilar da aka yi wa mabiyansa.