IQNA

Rundunar 'Yan Sanda London Ta Ce Ba Zata Amince Da Kin Jinin Musulmi ba

20:40 - June 13, 2017
Lambar Labari: 3481608
Bangaren kasa da kasa, babbar kwamishiniyar 'yan sanda a birnin London na kasar Birtaniya Cressida Dick ta ce ba zata taba amincewa da kyamar da ake nuna wa musulmi a birnin ba.
Kamfanin dillancin labaran iqna ya habarta cewa ya nakalto daga shafin Islamic News cewa, Cressida Dick kwamishiniyar 'yan sandan birnin London ta bayyana cewa, tun bayan kai harin da aka yi birnin kyamar da ake nuna wa msuulmi ta kazanta, wanda a cewarta ba za su amince da hakan ba, domin kuwa su kansu musulmi suna fuskantar barazanar ta'addanci.

Ta kara da cewa 'yan ta'addan da suka kai hare-haren London ba suna wakiltar musulmi ba ne, saboda haka babu dalilin da zai sanya a kyamci musulmi, domin manufar 'yan ta'adda ita ce raba al'umma da suke zaune lafiya da juna.

A lokacin da take maganada musulmi ta yi kira da cewa, a duk lokacin da musulmi suka ga wani a cikinsu da suke da tabbacin yana da alaka da kungiyoyin 'yan ta'adda ko kuma suke zarginsa da hakan, su gaggauta sanar da 'yan sanda, domin sai da hadin kan musulmi ne za a samu damar zakulo 'yan ta'adda da suke fakewa da sunan addinin suna aikata ta'addanci.

Cressida Dick ta kara da cewa, tun bayan harin London da aka kai 'yan kwanakin da suka gabata, kyamar da ake nunwa musulmi ta rubanya kusan sau biyar, abin da rundunar 'yan sandan London bat aba amince da shi ba.

3609369


captcha