Kamfanin dillancin labaran iqna ya bayar da rahoton cewa, a jiya an gudanar da zaman karatun kur’ani mai tsarki a babban masallacin ‘yan darikar Tijjaniya da ke fadar mulkin kasar Burkiya Faso, wanda wata cibiyar ‘yan shi’a karkashin jagorancin Tijjani samawi daga Tunisia ta dauki nauyin shiryawa.
Wannan taro dai na zuwa a daidai lokacin da ake gudanar ad taruka na watan sha’aban, domin shirin shiga watan Ramadan mai alfarma.
Kasar Burkina Faso dai tana daga cikin kasashen yammacin Afrika, kuma mafi yawan musulmin kasar mabiya darikar Tijjaniya ne.